
Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea ce ke rike da kofin zakarun Turai
Akwai yiwuwar za a hada kulob din Manchester United da kulob-kulob din da suka ci gasar champions league na Jamus da Spaniya da kuma Italiya, idan an tashi fitar da rukunan champions league a yau Alhamis.
Kulob din da ya lashe gasar Premier league wato Manchester City zai kasance a tukunya ta biyu kuma akwai yiwuwar karawarsu da Borussia Dortmund da Real Madrid da kuma Juventus.
Kulob-kulob din dake rike da kofunan gasar Champions wato Chelsea da Arsenal and Manchester United za su kasance a tukunya ta farko.
Kulob-kulob guda 32 ne za a zuba a tukwane hudu, sannan a raba su zuwa rukunai hudu dake kunshe da kulob-kulob takwas-takwas.
Kulob din da ya lashe gasar champions na Scottland wato Celtic, shi ma yana cikin rukunan da za a raba, saboda nasarar da ya samu a kan kulob din Helsingborgs.
Manchester City zai kasance a tukunya na biyu saboda nasarar da kulob din ya samu a gasar Uefa bai kai na tkwarorinsa dake tukunya ta daya ba.













