bbc.co.uk navigation

Man City ta sayi Rodwell daga Everton

An sabunta: 12 ga Agusta, 2012 - An wallafa a 20:01 GMT
jack rodwell

Jack Rodwell

Manchester City ta sayi Jack Rodwell daga Everton sai dai ba a bayyana yawan kudin cinikin ba.

Dan wasan mai shekaru 21 wanda Everton ta yi masa kudi fam miliyan 15 kocin Ingila ya zabe shi a cikin wadanda zasu bugawa kasar wasa a karawar da zata yi da Italiya ranar Laraba.

Ana ganin Rodwell zai karawa City karfi a tsakiya saboda rashin Gareth Barry wanda ya yi rauni a kugunsa da kuma rashin tabbas a game da Nigel de Jong a kungiyar saboda yana cikin shekarar karshe ta kwantiraginsa kuma kulob din Bayern Munich ya nuna sha'awarsa ta sayen dan wasan mai shekaru 27.

Rodwell ya fara wasa ne daga reshen matasa na kungiyar Everton tun yana shekara 7, kuma ya bugawa kungiyoyin matasa na kasar Ingila a matakai daban-daban har hudu kafin daga bisani ya fara bugawa babbar kungiyar 'yan wasan Ingilan a karawarta ta sada zumunta da Spain a watan Nuwamba na 2011.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.