bbc.co.uk navigation

Afrika ta kudu ta zayyana filayen gasar Afrika

An sabunta: 6 ga Mayu, 2012 - An wallafa a 16:26 GMT

Gasar cin kofin Afrika

Kasar Afrika ta kudu ta zayyana biranen da za'a yi amfani da filayen wasannin su don gasar cin kofin kwallon kafa ta nahiyar Afrika a shekara ta dubu biyu da goma sha uku.

Garuruwan dai sun hada da Nelspruiet da rustenburg da Port Elizabeth da Durban da kuma Johannesburg.

Wannan matakin na nuna cewar filin wasan Cape Town da aka gina shi don gasar cin kofin Duniya na shekara ta dubu biyu da goma ba za ayi amfani da shi ba a wannan gasar.

Filin wasan Johannesburg wanda ada ake kira Soccer City a inda akayi wasan karshe na gasar cin kofin kwallon kafa ta duniya , anan ne za'ayi wasannin budewa da kuma na karshe.

Kari a kan wannan labari

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.