bbc.co.uk navigation

Tevez zai dawo takawa City leda - Mancini

An sabunta: 23 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 13:25 GMT

Roberto Mancini

Kocin Manchester City Roberto Mancini, ya ce ya amince da ahuwar da Carlos Tevez ya nema, kuma dan wasan zai dawo taka leda nan da makwanni biyu zuwa uku.

Tevez dai ya bar kungiyar na tsawon watanni uku ba tare da izini ba, bayan dambarwar da ta kaure tsakaninsa da kocin kungiyar.

Tevez dai ya dawo kungiyar ne a makon daya gabata, kuma ya nemi ahuwa daga kungiyar da magoya bayanta.

Mancini dai ya ce ya kamata dan wasan ya yi horo sosai, kafin ya dawo taka leda gadan-gadan.

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.