bbc.co.uk navigation

Najeriya na neman karin haske daga Fifa

An sabunta: 21 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 15:41 GMT

Shugaban Fifa, Sepp Blatter

Hukumar kula da wasanni a Najeriya na fatan ziyaran da za ta kai gun shugaban Fifa Sepp Blatter a watan Maris, zai warware matsalolin da su ka addabi kwallon kafa a kasar.

A watan Junairu ne wata babbar kotun tarraya da ke Abuja ta ce ta russa Hukumar kula da kwallon kasar wato NFF da kuma Hukumar kula da gasar Premier a kasar wato NPL.

Kotun dai ta bayyana cewa Hukumar NFL da kuma NFA wato sunayen da ake amfani da su baya kadai ne ke da hurumin tafiyar da harkar kwallon kafa a kasar.

NFA dai ta sauya sunanta ne zuwa NFF a shekarar 2009 amma ta gaggara rajistar sunan kumar yadda doka ta tanada.

Wannan dalilan ne dai kuma ya sa dokar kasar ba ta amince da NFF a matsayin hallatacciyar hukumar da ya kamata ta tafiyar da harkar kwallon kafa a kasar.

Hukumar kula da harkar wasanni a Najeriya dai ta shigo cikin lamarin domin warware matsalar, abun da kuma yasa za ta tunkari Fifa domin samun karin haske.

Mai magana da yawun Hukumar, Mista Tony Ohaeri ya tabbatarwa BBC cewa hukumar za ta gana da shugaban Fifa a Zurich a ranar 15 ga watan Maris.

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.