bbc.co.uk navigation

Gagarumar tarba ga 'yan wasan Zambia

An sabunta: 13 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 15:44 GMT

'Yan kasar Zambia na can suna bukukuwan lashe gasar cin kofin kwallon kafa na kasashen Afrika.

An yi wa kungiyar kwallon kafa ta kasar gagarumar tarba a Lusaka babban birnin kasar bayan isowar su da kofin da suka lashe.

A daren jiya ne dai 'yan wasan Zambiyar suka doke Kot Divuwa a wasan karshe na gasar.

Wannan dai shine karon farko da suka lashe kofin kwallon kafa na kasashen Africa a tarihinsu.

An yiwa Kot Divuwa kallon wadda zata iya cin kofin tun ma kafun a fara gasar.

Wasan dai sai da ya kai bugun da ga kai sai gola, bayan da aka kammala wasan ana canjaras, duk kuwa da karin lokacin da aka yi.

Wani abu mai kara sosa zuciya a wurin yan kasar ta Zambia shine, an buga wasan karshen ne a birnin Libraville, inda wani hadarin jirgi da ya afku kusan shekaru ashirin da suka wuce, yayi sanadiyar mutuwar baki dayan yan wasan kwallon kafa na kasar ta Zambia a lokacin.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.