bbc.co.uk navigation

FA za ta tattauna a kan wanda zai gaji Capello

An sabunta: 9 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 15:54 GMT

Shugaban Hukumar FA, David Bernstein

Hukumar kwallon Ingila wato FA ta ce za ta tattauna a ranar Juma'a domin zabar wanda zai maye gurbin Fabio Capello, amma za ta fi maida hankali ne kan kocin mai jin Ingilishi kuma dan Burtaniya.

Shugaban Hukumar, ya ce hukumar na son maye gurbin kocin ne cikin gaggawa, amma ya ki ya ce uffan game da jita-jitan da ake yi cewa hukumar na zawarcin Harry Redknapp.

"Zamu yi abun da ya dace, kuma zamu fito da jerin sunayen wadanda muke so." In ji Bernstein.

Mataimakin kocin Ingila, Stuart Pearce ne zai jagoranci kasar a wasan sada zumuncin da za ta buga da Holland a ranar 29 ga watan Fabrairu.

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.