AFCON: Ghana ta doke Mali

An sabunta: 29 ga Janairu, 2012 - An wallafa a 14:01 GMT

'Yan wasan Ghana su na murnar zura kwallo

Ghana na kan hanyarta na tsallakewa zuwa wasan dab da kusa da na karshe a gasar cin kofin Afrika, bayan ta doke Mali da ci biyu da nema.

Asamoah Gyan ne ya fara zura kwallon farko a bugun falan daya bayan da aka dawo hutun rabin lokaci.

Andre 'Dede' Ayew kuma ya zura ta biyu inda ya tsame 'yan wasan bayan Mali kafin ya zura kwallon.

Mali dai su gamu da rashin sa'a domin dan wasanta Cheick Diabate ya yi kararrawa har sau biyu a sandan ragar Ghana.

Kasashen biyu sunyi taka tsan-tsan sosai a wasan kafin a tafi hutun rabin lokaci, saboda kowannen su na da kwarewa.

bbc.co.uk navigation

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.