QPR ta sayi Nedum Onuoha daga City

An sabunta: 26 ga Janairu, 2012 - An wallafa a 14:22 GMT

Nedum Onuoha asalin dan Najeriya ne

Kungiyar Queens Park Rangers ta kammala siyan dan wasan Manchester City Nedum Onuoha na tsawon shekaru hudu da rabi.

Dan wasan ya taka leda karkashin Mark Hughes a lokacin da yake horon kungiyar Manchester City.

Ya zuwa yanzu dai ba'a bayyana kudin da aka sayi dan wasan ba.

Dan wasan mai shekarun haihuwa 25, ya taka leda ne a kungiyar Suderland a kakar wasan bara na wucin gadi, saboda baya samu damar taka leda a City.

"Na san Nedum sosai, kuma dan wasa ne da zai taimakawa kungiyar sosai." In ji Mark Hughes.

"A lokacin da yake taka leda a karkashi na a kungiyar Manchester City ya taka rawar gani sosai.

"Kwareran dan wasan baya ne, kuma zamu iya amfani da shi ko ta wani bangare."

bbc.co.uk navigation

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.