Equatorial Guinea ta tsallake zuwa Q/Final

An sabunta: 26 ga Janairu, 2012 - An wallafa a 14:22 GMT

Daya daga cikin kasashen dake daukar nauyin bakuncin gasar cin kofin Afrika wato Equatorial Guinea ta tsallake zuwa zagayen wasan gab da kusa dana karshe.

Kasar dai ta bada mamaki ne bayan da ta doke Senegal da ci biyu da daya a wasanta na biyu.

A wasan farko da kungiyar ta buga ta doke Libya ne da ci daya mai ban haushi.

A yanzu haka dai an fidda Senegal a gasar, amma tana da sauran wasa daya.

"Gaskiya mun yi sa'a sosai muka zura kwallo dab da an kusan a tashi wasan. Muna da kwarin gwiwa zamu doke Zambia domin mu jagoranci rukunin da muke." In ji Juvenal Edjogo, kyaftin din Equatorial Guinea.

A daya wasan da aka buga a rukunin na A, Libya ce ta tashi biyu da biyu tsakaninta da Zambia.

bbc.co.uk navigation

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.