|
Sabuwar Majalisa a Niger
|
||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
A Jamhuriyar Niger an kaddamar da sabuwar majalissar dokokin kasar karkashin sabuwar Jamhuriyar da Shugaba Malam Tandja Mamadou
ya bullo da ita, wadda ta bashi damar zarcewa akan karagar mulki.
Wannan majalissar dokoki ita ce ta farko a karkashin jamhuriya ta 6. Majalissar ta kunshi yan majalissu 113 da suka hada da mata 11. Jam'iyyun adawa na Niger sun kauracwa zaben yan majalissar dokokin suna cewar ya sabawa doka. Kungiyar Ecowas ko Cedao ta dakatar da jamhuriyar Niger daga cikin kungiyar a sakamakon gudanar da zaben yan majalissar dokokin. An kaddamar da majalissar ce a lokacin da kungiyar Ecowas ke tattaunawa da bangarorin siyasar Niger da nufin warware rikicin
siyasar da ake fama da shi. |
|||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
|
|||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
|
|||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||