BBCHausa.com
Inglishi
Larabci
Faransanci
 
An sabunta: 14 Nuwamba, 2009 - An wallafa a 15:03 GMT
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
Sabon Zargi kan Sojojin Burtaniya
 
Basra
Sojojin Birtttania a Basra
Ma'aikatar harkokin tsaro ta Birtaniya ta ce tana gudanar da bincike akan wani sabon zargi da ake yiwa sojojin kasar cewar sun ci zarafin wasu mutane a Iraqi, lokacin da yankin Basra ke hannunsu.

Lauyoyin da ke wakilatar mutanen da aka ci zarafi sun bayyanawa jami'an Birtaniya kararraki na cin zarafi har guda talatin da uku wadanda suka ce sun bayyana tun bayan da dakarun Birtaniya suka janye daga Basra a watan Yuni.

Daya daga cikin zargin ya shafi fyaden wani yaro dan shekaru 16 da wasu sojojin Birttaniya 2 suka yi.

Lauyoyin sun yi kiran a gudanar da cikakken bincike na bainar Jama'a akan wannan zargi.

 
 
KA KUMA DUBA
 
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
 
  Game da mu|Tuntube mu
 
BBC Copyright Logo
 
^^ Koma sama
 
  Labarai | Yanayi
 
  BBC News >> | BBC Sport >> | BBC Weather >> | BBC World Service >> | BBC Languages >>
 
  Taimako | Tuntube mu | Tsare Sirri