|
China zata ba kasashen Afirkar da suka fi fama da talauci, wasu sabbin basusukan da suka kai dala bilyan goma, a shekaru ukku
masu zuwa. Gwamnatin Chinar zata kuma yafe wasu basusukan da take binsu.
Praministan kasar ta Sin ne, Wen Jiabao, yayi sanarwar a taron kolin da Chinar ke yi da kasashen Afirka, a wurin shakatawa
na Sharm El Sheikh da ke kasar Masar.
Da ma dai China ta zuba jari na biliyoyin daloli a kasashen Afrikar, amma tana shan suka, kan yadda take yin biris da batutuwan
tauye hakkin jama'a, a kokarinta na samun albarkatun da Allah ya horewa nahiyar Afirkar.
|