|
Taron G20 A Scotland
|
||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
|
Ministocin kudi na kasashen duniya guda ashirin da suka fi karfin tattalin arziki (G20) na taro a St Andrews, Scotland, don
tattaunawa a kan batun farfadowa daga matsalar tattalin arzikin da duniya ta fada ciki da kuma kudin da ake bukata don magance
matsalar sauyin yanayi.
Yayin da tattalin arzikin duniya ke kara samun daidaito a 'yan watannin nan, masu zuba jari da dama na kara zuba jari a kasuwannin hada-hadar kudade na kasashe masu tasowa. Wannan na faruwa ne sakamakon kwarin gwiwa da masu zuba jarin su ke sake samu da kuma rage kudin ruwa da manayan bankuna suka yi a kasashe masu wadata. Sai dai wannan ya sa wasu kasashe masu tasowa sun fara nuna damuwa. Kwararowar wadannan kudade ya sa darajar kudaden kasashen masu tasowa ta hauhawa, abin da ke sa masu shigo da kaya na kasashen suna shan wahala. Ana kuma nuna damuwa a kan yiwuwar wannan al'amari ya zama wani sabon sanadin afkawa matsalar tattalin arziki a duniya. |
|||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
|
|||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
|
|||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||