 |
|
| Hasumiyar Majalisar Dokoki Ta Najeriya |
Majalisar Wakilan Najeriya ta yi barazanar cewa ba za ta amince da duk wani kason da bangaren zartarwa zai nemi kebewa shirin
muradun karni (MDGs) ba a kasafin kudin shekara mai zuwa.
Wasu 'yan Majalisar dai sun ce bai kamata a kebewa shirin ko da sisin kwabo ba, tunda har yanzu ofishin da ke gudanar da shirin,
wanda ke Ofishin Shugaban Kasar, bai kammala aiwatar da wasu ayyukan kasafin kudin shekara ta 2008 ba.
Honorabul Labaran Yunusa Dambatta ya shaidawa wakilin BBC cewa 'yan Majalisar sun yanke wannnan shawara ne don bin kadin hakkin
jama'a.
"An sa [ayyukan da ofishin MDGs din ke yi] a cikin kasafin kudin shekarar 2008, wadanda yanzu haka ana yi, da dama ba a gama
ba. Saboda haka mu ke ganin lallai ya kamata a ce an gama wadannan. Na bana kuma, wato 2009, har yanzu ba a fara ba", inji
Honorabul Dambatta.
|