BBCHausa.com
Inglishi
Larabci
Faransanci
 
An sabunta:
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
Bangarorin Siyasar Niger Zasu Tattaunawa Abuja
 
Mamadou Tanja
Shugaba Mamadou Tanja na Niger
Bangarorin siyasa masu hamayya da juna a jamhuriyar Niger na shirye-shiryen zuwa Nigeria, domin tattaunawar neman kawo karshen rikicin, a karkashin kungiyar ECOWAS ko CEDEAO, ta kasashen yammacin Afirka.

An dai shiga rikicin siyasa ne a kasar ta Niger, tun bayan da Shugaba Tanja ya kuduri aniyar zarcewa da mulki, duk da cewa kundin tsarin mulkin kasar ya haramta masa yin hakan.

A makon gobe ne ake shirin yin tattaunawar a Abuja, a karkashin jagorancin tsohon shugaban mulkin sojan Nigeria, Janar Abdussalami Abubakar mai ritaya, wanda kungiyar ECOWAS ta nada a matsayin mai shiga tsakani.

Dukan bangarorin siyasar Niger din sun ce zasu halarci ganawar.

 
 
KA KUMA DUBA
 
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
 
  Game da mu|Tuntube mu
 
BBC Copyright Logo
 
^^ Koma sama
 
  Labarai | Yanayi
 
  BBC News >> | BBC Sport >> | BBC Weather >> | BBC World Service >> | BBC Languages >>
 
  Taimako | Tuntube mu | Tsare Sirri