|
A yau ministoci da kuma jamian tsaro na kungiyar kasashen yammacin Afrika, watau ECOWAS ko CEDEAO, suka fara wani taro a
Abuja, domin samar da hanyar da za su inganta tsaro a kan iyakokinsu .
Taron zai duba hanyoyin daukar matakan magance matsalolin safarar miyagun kwayoyi da safarar mutanen dake addabar yankin
.
Mahalata taron za su kuma yi nazari a kan shawarwarin da jami'an tsaro na kungiyar suka bayar, a kan kafa wata rundunar
ko-ta -kwana a yankin.
A farkon wannan makon ne jamian tsaron yankin da suka hada shugabanin yansanda suka gudunar da wani taron akan wanan
batu
|