 |
|
| Firaministan Birtaniya Gordon Brown |
Firaministan Birtaniya, Gordon Brown yace Birtaniya zata cigaba da horar da dakarun tsaro na Afghanistan, duk da kashe sojojinta
biyar da wani dan sandan Afghanistan ya yi.
Mr. Brown ya shaidawa majalisar dokokin Birtaniya cewa, kungiyar Taleban tace ita ke da alhakin kai harin, sai dai
kuma ba'a san ko sun shiga cikin 'yan sandan ko kuma sun yi amfani da jami'an su ba ne.
Wakilin BBC yace tun kimanin makwannin biyun da suka wuce sojoji ke tare da 'yan sandan Afgahnistan din domin basu horo
a lardin Helmand. Sojojin Birtaniya da 'yan sandan Afghanistan din da dama sun jikkata a hari.
|