BBCHausa.com
Inglishi
Larabci
Faransanci
 
An sabunta:
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
Tawagar Gwamnatin Niger Zata Gana da Shugabannin Nigeria
 
Wata tawaga ta jami'an gwamnatin Nijar ta isa babban birnin Tarayyar Nigeria, Abuja, domin ganawa da mahukuntan kasar, ciki har da Shugaba Umaru Musa 'Yar Adua.

Masu nazari dai na hasashen cewa, ziyarar ba zata rasa nasaba da irin wadda jami'an Niger din suka kai a kwanan baya ba a kasashen yammacin Afrika, renon Faransa, tun bayan da kungiyar tattalin arzikin yammacin Afrika ta ECOWAS ko CEDEAO, ta dakatar da kasar daga cikinta.

Tuni Tarayyar Afirka ta goyi bayan matakin da CEDEAO din ta dauka a kan Niger, tare da yin kira a gareta da ta koma mulkin demokradiyya na zahiri.

 
 
KA KUMA DUBA
 
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
 
  Game da mu|Tuntube mu
 
BBC Copyright Logo
 
^^ Koma sama
 
  Labarai | Yanayi
 
  BBC News >> | BBC Sport >> | BBC Weather >> | BBC World Service >> | BBC Languages >>
 
  Taimako | Tuntube mu | Tsare Sirri