BBCHausa.com
Inglishi
Larabci
Faransanci
 
An sabunta:
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
Niger na Neman Sulhu da Makwabtanta
 
Wata tawagar jami`an gwamnatin janhuriyar Nijar,t a gana da shugaban Najeriya Umaru Musa `Yaradua yau a Abuja.

Tawagar ta hada da Firaministan jamhuriyar Nijar da wasu jami'an gwamnati da dama, wadanda suka je Najeriyar don neman goyon bayan a sassauta wa Niger din dangane da dakatarwar da kungiyar ECOWAS ko CEDAO tai mata.

A bayan ganawar tasu, tsohon shugaban Nigeria kuma jagoran dake shiga tsakani a rikicin siyasar Niger, janar Abdussalam Abubakar yace tawagar tazo ne domin neman Nigeria ta shiga tsakanin wajen warware rikicin siyasar Niger din.

A kwanakin baya ma tawagar ta kai irin wannan ziyarar kasashen yammacin Afirka renon Faransa.

 
 
KA KUMA DUBA
 
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
 
  Game da mu|Tuntube mu
 
BBC Copyright Logo
 
^^ Koma sama
 
  Labarai | Yanayi
 
  BBC News >> | BBC Sport >> | BBC Weather >> | BBC World Service >> | BBC Languages >>
 
  Taimako | Tuntube mu | Tsare Sirri