 |
|
| Shugaba Hamid Karzai |
Hukumar zaben Afghanistan ta soke zagaye na biyu na zaben shugaban kasar, kuma ta bayyana shugaba Hamid Karzai a matsayin
wanda ya lashe zagayen farko na zaben.
Kakakin hukumar zaben ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai.
Sakataren majalisar dinkin duniya Ban Ki-Moon ya yi maraba da wannan mataki, sannan ya taya Mr Karzai murna.
Wakilin BBC ya ce, yanzu shugaba Hamid Karzai zai cigaba da zama a kan karagar mulki. Hakan dai ya biyo bayan janyewar da
abokin hamayyarsa, Abdullah Abdullah ya yi ne, yana mai cewa, za a iya maimaita magudin da aka tafka a zagayen farko.
|