BBCHausa.com
Inglishi
Larabci
Faransanci
 
An sabunta: 12 Disamba, 2007 - An wallafa a 20:16 GMT
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
Demokaradiyya A Najeriya
 
 Mutane na kan layin kada kuri'a
Mutane na kan layin kada kuri'a
Shirye Shirye na Musamman Kan Cikar Shekaru Goma Da Maido Da Mulkin Demokaradiyya A Najeriya Ba Tare Da Sirkin Mulkin Soji Ba.

Tsarin democradiyya na nufin gwamnati ta mutane wadda jama'a ke yankewa kansu shawara kan wanda zai wakilce su ko kuma ya shugabance su. Wannan wani tsari ne da jama'a ke da 'yanci ta fuskar siyasa wanda ya dogara kan tsarin gudanar da gasa ta zabe kuma bisa gaskiya. A cikin shekaru 10 da suka shige Nigeria tana bin tsarin democradiyya, abunda ake ganin gagarumin ci gaba ne domin shine lokaci mafi tsaho da aka samu mulkin farar hula tun bayan da kasar ta karbi 'yancin kai daga Birtaniya a 1960. Daga ran 1 ga watan Mayun shekarar 2009 ne Sashen Hausa na BBC ya fara gabatar muku da rahotanni da hirarraki na musamman, kan shekaru goma da Nigeria ta yi tana bin tsarin democradiyya ba tare da surkin mulkin soja ba - abunda kuma zamu shafe wata guda muna yi. A wannan shafi za kuji jerin rahotanni inda muka duba nasarorin da aka samu da kuma kalubalen dake gaban Nigeria a yunkurin ta na tattabar ci gaba da kasancewa bisa wannan tafarki da masanan kimiyyar siyasa na duniya suka bayyana da cewa yana da matukar riba ga al'umma.

 Siyasa rigar yanci, amma a Najeriya rigar cin hanci ne da rashawa.
 
Sani Yakubu Yayarin Tukur a Jigawan Najeriya

1 Ga Watan Mayu 2009

Tsarin na dimukradiyya dai tsari ne mai manufa ta bai daya a sassa dabam dabam a duniya. Sai dai wajen aiwatar da shi ne ake samun bambanci, musamman ma akan yadda 'yan siyasa da mahukunta ke ganinsa.

 Abinda ya burgeni a demokaradiyyar Najeriya shine yadda aka maida sojoji barikokinsu
 
Ari Wagani Bosso, Najeriya.

2 Ga Watan Mayu 2009

Tun lokacin da kasar ta sami 'yancin kai kusan shekaru arba'in da tara da suka wuce, a lokuta dabam-dabam an yi wa mulkin demokradiyyar karan tsaye, sakamakon juye-juyen mulkin da sojoji suka rika yi.Ga shirin Gane Mani Hanya na mussaman akan cikar shekaru goma da dorewar mulkin demokradiyya a Nijeriya .

 Ina son jama'a ku gane ba dole bane wanda kuka zaba ya ci zabe , idan har kuri’ar ku bai fa da bangaren masu rinjaye ba
 
Abdu Makama Maiduguri Najeriya.

3 Ga Watan Mayu 2009

Shirinmu na Taba Kidi Taba Karatu na wannan makon an gabatar dashi ne kacokan akan mulkin demokaradiyyar Najeriya.

 Matsalar siyasar Najeriya itace kin amincewa da sakamakon zabe mussaman wanda ya fadi
 
Baballe Musa Fagge Kano Najeriya

4 Ga Watan Mayu 2009

Wani bangaren da ake ganin ya kamata ya ci gajiyar mulkin demokradiyyar shine: yankunan karkara, wadanda bisa tsarin mulki ke karkashin kananan hukumomi.
Bayan an kwashe shekaru goma ana mulkin demokradiyya ba tare da wata tangarda ba da alamun har yanzu mazauna karkara basu gani a kasa ba, ganin irin koke-koken da ke fitowa daga yankunan mussaman akan batunnan na wani asusun hadin gwiwa da jihohi.

 Matasa Najeriya mu farga mu daina shi ga bangar siyasa don cigaban kanmu da kasarmu
 
Hassan Aliyu Kwarbai Najeriya

5 Watan Mayu 2009

Tun lokacin da Najeriya ta sami 'yancin kai kusan shekaru arba'in da tara da suka wuce, a lokuta dabam-dabam an yi wa mulkin demokaradiyyar karan tsaye, sakamakon juye-juyen mulkin da sojoji suka rika yi. Shekaru goman da aka yi a jere ana mulkin farar hula a Najeriya shi ne mafi tsawo a tarihin kasar. Kokarin da aka yi a karo na farko da na biyu da na ukku basu yi karko kamar na wannan karon ba. Wannan ne ya baiwa 'yan kasar da dama kwarin gwiwar yin hasashen samun habakar demokaradiyya a kasar, duk kuwa da irin matsalolin da tsarin ke fuskanta.

 Shekaru goma da aka koma mulkin demokaradiyya a Najeriya, talakawa dai har yanzu jiya iyau
 
Bello Koko Yaron Yusuf Najeriya

6 Ga Watan Mayu 2009

Rawar da Shugabannin gwamnati ke takawa a tsarin mulki irin na demokaradiyya na da muhimmanci ga cigaban rayuwar 'yan kasa da tattalin arzikin kasar. To amma a Najeriya, duk da cewa kasar ta shafe shekaru goma kan turbar demokaradiyya, rashin kyakkyawan Shugabanci ne masana harkokin siyasa suka ce Ummul-haba'isin matsalolin da kasar ke fuskanta. Nijeriya dai kasa ce dake bin tsarin siyasa mai matakai uku na gwamnati, to amma, masana harkokin siyasa, sun bayyana cewa dukkan Shugabannin matakan gwamnatocin kasar, suna yin karan-tsaye ga tanade-tanaden tsarin na demokaradiyya, abinda shugabannin suke musantawa. To kowacce rawa ya kamata Shugabannin a matakan gwamnatocin ukku su taaka? Ina kuma masu tsawatawa musu da ake batun suna saba ma tsarin na demokaradiyya?

 Ya kamata gwamnatin tarrayya ta kyautata harkar zabe a Najeriya don talakawa su ci ribar dimokaradiya a kasar
 
Muhammad Sani Kontagora Najeriya.

 Demokaradiyyar Najeriya, shekaranki goma kina rarrafe, amma kin kasa tashi, muna fatar Allah ya gyara zukatan masu renonta ko zata mike
 
Mahmood Hamma Misau Bauchi Najeriya.

7 Ga Watan Mayu 2009

Tun daga lokacin da aka yi nasarar kawar da mulkin soja a Najeriya ne, wato shekaru goma da suka wuce, 'yan kasar suke cin moriyar mulkin farar hula. Duk da korafin da wasu ke yi na cewa 'yan siyasa sun kasa magance matsalolin kasar, akasarin 'yan Najeriyar na nuna cewa mulkin dimukradiyyar ne suke bukata.

 Shugabannin Najeriya kusani fa akwai gobe kiyama
 
. Sahabi Muhammed Mai wanki hula Najeriya

 Najeriya ya kamata ki yi koyi ga kasar Indiya saboda tafiki yawan jama’a amma ta gunadar da zabe babu tashin hankali , saboda haka ne zai habbaka mulkin demokaradiyya
 
Siraj Muhammed Sani Zungeru, New Delhi, Indiya

8 Ga Watan Mayu 2009

Jam'iyyun siyasa sune shika-shikan kafa gwamnatin dimukradiyya. Akwai fiye da jam'iyyu hamsin a Najeriya, amma kalilan daga cikin sune keda kujerun mulki ko na wakilci a majalisun dokokin kasar. Wasu daga cikin jam'iyyun sun samo tushe ne daga tsaffin jam'iyyun siyasar kasar, amma yawancinsu, an kafa sune a cikin 'yan shekarun nan. Masana da dama na ganin cewa batun akida ya gushe a tsarin jam'iyyun kasar.

 Shekaru goma da tsarin damokaradiya a Najeriya mu dai talakawa sai muce har yanzu kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba
 
Mathew Garba Maiduguri Najeriya

9 Ga Watan Mayu 2009

Gudanar da zabukan cikin gaskiya da adalci na daga cikin abubuwan da ke kawo inganci a tsari irin na mulkin demokaradiyya, saboda hakan zai baiwa masu zabe damar kafa irin gwamnatin da suke so da zata ja ragamar mulkin a inda suke. Shirin Gane Mani Hanya na wannan makon ya nazari akan yadda yakamata zabuka su kasance a Najeriya

 Mu dai ala san barka, saboda a mulkin demokaradiyyar Najeriya, ko babu komai muna da ‘yancin fadin albarkacin bakinmu
 
Hassan Alkali Gusau Zamfara Najeriya

11 Ga Watan Mayu 2009

Wani babban abinda ke bambanta mulkin soji da na farar hula shi ne wanzuwar majalisun dokoki. A tsarin dimukradiyya dai hakkin majalisun dokokin ne su kafa sabbin dokoki; su gyara wadanda ba'a gamsu dasu ba; su kuma sa-ido ga abubuwa da jami'an gwamnati ke yi, don tabbatar da ganin cewa ba a ci amanar jama'a ba. To, ko majalisun dokokin Najeriyar na yin hakan a shekaru goma na wannan mulkin farar hular?

 Mu ’yan Najeriya shekaru goma ana demokaradiyya amma bamu san inda aka sa gaba ba. Fatarmu dai shine Allah ya zaban mana shugabanni nagari
 
Abbas Sabitu Chuwasu Jigawa Najeriya

12 Ga Watan Mayu 2009

Yawan zarge-zargen cin hanci da rashawa na daga cikin matsalolin da suka addabi majalisar dattawan Najeriya a shekaru goma na wannan mulkin farar hular. A kan hakan nema wasu daga cikin shugabannin majalisar suka rasa mukamansu; wasu 'yan Najeriya kuma su ka yi zargin cewa mutuncin majalisar ya zube. 'Yan majalisar dattawan dai sun sha musunta hakan, wasunsu kuma na danganta rigingimun shugabancin majalisar ne akan tsoma bakin bangaren zartarwa.

 Ina kira ga ‘yan siyasa su bar talakawa su zabi wanda su ke so don suma su ci ribar demokaradiyya
 
Bako Zinder Jamhoriyar Nijar

13 Ga Watan Mayu 2009

Gudanar da bincike na daya daga cikin ayyukan da tsarin mulkin Najeriya ya tanadarwa 'yan majalisun dokokin kasar. Majalisar wakilai data dattawan kasar suna nuna cewa sun dukufa wajen wannan aiki. To saidai 'yan Najeriya da dama na korafin cewa har yanzu hakan bai haifar da komai ba. Wasu ma na zargin cewa neman cimma burin siyasane kesa ake kafa wasu kwamitocin binciken

 Matukar ba’a daina siyasar uban gida ba a Najeriya, a ganina siyasarmu ba zata taba ci gaba ba, saboda masu mulki zasufi fifita iyayen gida a maimakon talakawa
 
Nuhu Ibrahim Hausari a Barno Najeriya.

14 Ga Watan Mayu 2009

Babban kalubale ga mulkin dimukradiyya a Najeriya shine batun gudanar da sahihin zabe a kasar. Kusan anyi amannar cewa tunda aka sake komawa mulkin farar hula shekaru goma da suka wuce, an kasa gudanar da sahihin zabe a kasar. Rashin gudanar da sahihan zabene ke haddasa yawancin rigingimun siyasar kasar, ya ke kuma bata mata suna a idon duniya. Gwamnati na batun gyara tsarin gudanar da zabe a kasar, amma wasu na ganin cewa gyaran bai kai yadda ake bukata ba.

 Rashin adawa ce babbar matsalar demokaradiyya a Najeriya bayan shekaru goma da kafuwanta. Saboda haka ya kamata ‘yan siyasa su canza salo
 
Zayyanu Alawaddu a Birnin Kebbi Najeriya

15 Ga Watan Mayu 2009

Daya daga cikin sauye sauyenda ake son yiwa tsarin gudanar da zabe a Najeriya shine baiwa dan takara mai zaman kansa, wato indipendaa, damar tsayawa zabe. A dokokin zaben da ake amfani dasu yanzu dai, jam'iyyun siyasa ne kawai ke da ikon tsaida mutum takara, to amma yanzu gwamnatin kasar na neman sauya hakan domin baiwa 'yan takara masu zaman kansu 'yancin yin takarar mukamai tun daga na majalisar dokoki har ya zuwa kujerar shugaban kasa.

 Muna farin cikin cikar Najeriya shekaru goma a mulkin demokaradiyya amma dai har yanzu akwai sauran rina a kaba
 
Garba Lawal Danmusa a Najeriya

16 Ga Watan Mayu 2009

Wani batu dake jan hankalin ‘yan Najeriya a wannan lokacin na mulkin demokaradiyya shine batun yadda jam’iyyun siyasa ke gudanar da harkokinsu mussamman ta yadda ake tsayarda ‘yan takara da kuma batun tarukan da ake zaben shugabannin jam’iyya, inda a lokuta da dama ake zargin cewar masu riko da mukamman gwamnati kan yi amfani da kujerunsu wajen nada wadanda suke so, abinda suka sha musantawa.

 ‘Yan Najeriya sai muyi ta addu’a, don kuwa demokaradiyyar kasar mu ta zama motar kwashe kaya wacce ta sha gangara babu direba balle birki, abin sai dai muce Allah gamu gare Ka
 
Torno Umaru Talire Gombi Jihar Adamawan Najeriya

18 Ga Watan Mayu 2009

A harkar gudanar da mulki a Najeriya, hakkin majalisun zartawar ne su aiwatar da tsare-tsaren gwamnati, majalisun dokoki kuma su sa ido ga abinda ke wakana. Manyan ayyukka na kasa sun dogara ne a kan majalisar zartawa ta tarayya, karkashin jagorancin shugaban kasa. Hakkin ministoci ne da sauran makarraban gwamnatin tarraya su gudanar da ayyukan da shugaban kasa ya basu, a kan yadda tsarin mulki ya shimfida. A shekaru goma da sake kafa mulkin farar hula ba yankewa a Najeriyar, jami'an gwamnatin tarayya sun dade suna ikirarin cewa ana aiwatar da tsarin bisa ka'ida, to amma 'yan kasar da dama na nuna tababa a kan hakan.

 Shekara goma ana mulkin demokaradiyya a Najeriya, amma har yanzu ‘yan kasar ba suda cikakken ikon zaben wadanda suke so su shugabancesu
 
Alhaji Abdullahi Mai Gora a Zariya

19 Ga Watan Mayu 2009

Tun komawar Najeriya ga mulkin Demokaradiyyane majalisun Dokokin kasar ke yunkuri daban-daban don gyaran-fuska ga kundin tsarin mulkin kasar amma babu wanda ya yi nasara. A baya-bayan nan ma majalisun dokokin kasar sun yi kamar za su yi, amma sai maganar ta lafa. Ko a ina matasalar take?

 Allah yasa a cigaba da mulkin demokaradiyya a Najeriya kuma shugabanni su daina handame kudin kasa.
 
Bilya Romo Bakwai Kano Najeriya

20 Ga Watan Mayu 2009

Abu ne da ya zama al`ada a duk lokacin da wata kasa ke gudanar da zabe, ayarin `yan sa-ido kan yi tururuwa zuwa kasar don duba yadda zaben ke gudana. A Najeriya ma ayarin masu sa-ido na kasa da kasa sun ziyarci kasar a manyan zabubbukan da ta gudanar a cikin shekaru goma da komawarta ga mulkin Demokuradiyya.

 To ‘yan Najeriya sai mu rika yin addu’a ga shugabanninmu da muka zaba ko za suyi mana adalci saboda dai adawa da kuma kace nace ba zasu magance mana matsalolinmu ba
 
Kabir Abba Nadakila Katsina Najeriya

21 Ga Watan Mayu 2009

A cikin shekarun goman da suka shige, Najeriya na fuskantar kalubale daban-daban a yunkurin kasar na tabbatar da dorewar tsarin da masana kimiyyar siyasar duniya suka yi imanin shi ya fi dacewa ga ci gaban al'umma - wato tsarin democradiyya. Daya daga cikin manyan kalubalen demokaradiyya a Najeriya a wadannan shekaru kuwa, ita ce siyasar yanki ko salon karba karba wajen rabon mukamai, abunda wasu ke ganin yana tauye manufar demokaradiyya.

 Shekaru goma cifcif, da demokaradiya a Najeriya amma abin takaici, har yanzu talaka ya kasa samun cigaban da ya kamata
 
Garba Usman Jakusko Gashua Najeriya

22 Ga Watan Mayu 2009

Cin Hanci da rashawa na daga cikin munanan abubuwan da tsari irin na demokaradiyya ke kokarin kawarwa. Ganin cewa yanzu haka an shafe shekaru goma kenan Najeriya na kan tsarin demokaradiyya, to ko yaya matsalar ke hana ruwa gudu?

 Matsalar 'yan siyasar Najeriya itace alkawari ba cikawa, saboda haka talakawa sai mukoma ga Allah
 
Ali Yunusa Shargalle Dutsi Katsina Najeriya

23 Ga Watan Mayu 2009

Matsalar zargin cin hanci da rashawa ga shugabanni na daga cikin dinbim matsalolin da suka da baibaye harkokin siyasar Najeriya a cikin shekaru goma da kasar ta kwashe tana gudanar da mulkin demokaradiyya babu kakkautawa, kuma shirin Gane Mani Hanya na wannan makon yayi nazari ne akan wannan matsalar.

 Hakika munga cigaba sosai a shekaru goma na mulkin demokoradiyya a Najeriya, Allah yasa gaba tafi inda aka fito
 
Injiniya Bello Fari Alaba Rago Legas Najeriya

25 Ga Watan Mayu 2009

Batun sarrafa dukiyar kasa na daga cikin manyan abubuwan da ke kan gwamnatin tarayyar Najeriya. Tsarin mulki ya dora manyan ayyukan kasa ne a kan gwamnatin tarayyar, domin itace ke da kaso mafi girma na dukiyar kasar.
A shekaru goman da suka gabata, gwamnati ta samu kudaden shiga masu yawa. Yayinda wasu 'yan kasar ke zargin cewa ana almubazzaranci da kudaden ne, jami'an gwamnati na nuni da cewa ana kashe kudaden ne ta hanyar da ta dace. Hakkin 'yan majalisun dokokin kasar ne dai takawa bangaren zartawa birki don hana alfasha da dukiyar jama'a.

 ‘Yan Najeriya mu rinka yiwa shugabanninmu addu’a a memakon jafa’in da akan yi musu
 
David L.T. Yolde karim Lamido Taraba Najeriya

26 Ga Watan Mayu 2009

Tun komowarta ga tafarkin demokaradiyya gwamnatin Najeriya ta fito da shirin samar da ilimi na bai daya, wato UBE ne da nufin wadata illahirin yaran kasar da ilimin firamare da kuma na karamar sakandare nan da sherara ta dubu biyu da goma sha biyar. Gwamnatin kasar dai na kashe dubban miliyoyin nairori a kan shirin don cimma wannan buri. Sai dai masana na cewa zaiyi wuya Najeriyar ta samu biyan bukata, sakamakon abin da suka bayyana da rashin kyakkyawan shiri.

 Shekaru goma ana mulkin demokaradiyya a Najeriya , amma har yanzu ba ruwa, ba wuta, ba taki ga manoma, ba magani a asibitoci sannan kuma ga talauci a cikin al'umma
 
Yusuf Rafin-Dadi Katsina Najeriya

27 Ga Watan Mayu 2009

A Najeriya cikin shekaru goman da kasar ta yi da komawa ga mulkin demokuradiyya, gwamnatin kasar ta kai turakun wutar lantarki a birane da yankunan karkara masu yawa. Sai dai kuma al`ummar kasar na kukan cewa ba su taba fuskantar matsalar karancin wutar lantarki irin na wannnan lokaci ba. Gwamnatin Najeriyar ta sha yin alwashin magance matsalar tare da kashe makudan kudade, amma har yanzu al`umomin kasar da dama na cikin duhu.

 ‘Yan Najeriya kusani cewar in bera da sata to daddawa ma da wari, don haka talakawa mu gyara halayenmu kafin zabe mai zuwa
 
Sani Ahijo Argungu Najeriya

28 Ga Watan Mayu 2009

Batun gudanar da sahihin zabe a Najeriya shine kalubale mafi girma a shekaru goman da aka shafe bayan maido da mulkin dimukradiyya a kasar. Akasarin 'yan Najeriyar sun yi amannar cewar ba a gudanar da sahihan zabuka a kasar yanzu. Sai dai duk da haka akwai wasu zabukan da aka yi a kasar inda 'yan kasar suka daage suka kaare kuri'unsu. Wannan ne ma ya kawo batun taken da ake kira: "a kasa, a tsare, a raka", wanda wasu ke nuni da cewa anyi a Jihar Bauchi. Ko hakan zai taimaka wajen kawo gyara a tsarin zabe a Najeriya?

 Duk da kwashe tsawon shekaru goma ana mulkin demokaradiyya a Najeriya amma har yanzu kasar na fama da yunwa da kuncin rayuwa
 
Abullahi Usama Song Nnewi Najeriya

29 Ga Watan Mayu 2009

A Najeriya yau ake bikin ranar demokaradiyya, wato ranar da shekaru goma da suka wuce kasar ta koma bisa tafarkin siyasar demokaradiyya. A kokarin kitse jerin rahotanni da shirye shirye na musamman da Sashen Hausa na BBC ke gabatar muku duk tsawon watan nan na Mayu, a halin yanzu zaku saurari tattaunawa ta musamman akan ita kanta siyasar demokaradiyya da irin fadi tashin da aka yi ta fama da shi a cikin shekaru goman da suka wuce.

 Allah ya nuna mana ranar da talakan Najeriya zai ji shima ana damawa da shi wajen cin moriyar dinbim arzikin da Allah ya huwace wa kasar
 
Yunus Umar Jawando Wase Filato Najeriya

30 Ga Watan Mayu 2009

Yanzu dai shekaru goma kenan da komawar Najeriya ga mulkin demokaradiyya ba kakkautawa amma dai jama`ar kasar na kukan cewa ba su ga wani sauyi a rayuwarsu ba. Masana dai na danganta wannan matsala da gazawar shugabanni wajen kyautata rayuwar al`umar kasar. Daga shekarar 1999 zuwa yanzu dai Najeriyar ta gudanar da manyan zabubbuka a kasar har sau uku, amma dukkansu masu sa-ido a kan harkokin zabe sun yi zargin cewa suna cike da magudi, al`amarin da masana ke cewa na matukar barazana ga dorewar dimukuradiyya a kasar. Shirin Gane Mani Hanya ya maida hankali ne akan makomar demokaradiyya a Najeriya.

Za ku iya tuntubarmu da ra’ayoyi ko shawarwarinku ta hanyar adireshinmu na e-mail wato hausa@bbc.co.uk

 
 
WASU SHAFUNAMMU
BBC Hausa A Karkara
20 Afrilu, 2007 | News
Rahoto Cikin Hoto
20 Afrilu, 2007 | News
KA KUMA DUBA
 
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
 
  Game da mu|Tuntube mu
 
BBC Copyright Logo
 
^^ Koma sama
 
  Labarai | Yanayi
 
  BBC News >> | BBC Sport >> | BBC Weather >> | BBC World Service >> | BBC Languages >>
 
  Taimako | Tuntube mu | Tsare Sirri