BBCHausa.com
Inglishi
Larabci
Faransanci
 
An sabunta: 01 Satumba, 2009 - An wallafa a 19:10 GMT
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
Shirin Yamma
 
Gaza
Gaza

Kwamitin gudanar da bincike na MDD yace Isra'ila ta tabka muggan laifuka, kuma ta karya dokokin kasa da kasa kan hakkin bil-adama, a lokacin da ta kaddamar da hare hare a Zirin Gaza a farkon wannan shekarar.

Kwamitin binciken wanda mai shigar da kara, Richard Goldstone ya jagoranta, yace da gayya dakarun sojin Isra'ila suka kai hari kan Palasdinawa fararen hula da gine ginansu.


An harba makamai masu linzami da dama zuwa cikin wani bangare da ake kira Green Zone a tsakiyar birnin Bagadaza, a dai dai lokacin da mataimakin shugaban kasar Amurka Joe Biden ke yin wata ziyara a kasar.

'Yan sanda a Iraqin sunce makamai mazu linzamin biyu sun fada dab da ofishin jakadancin Amurka. Yanzu haka babu rahotannin dake nuna wadanda harin ya ritsa dasu.

Gabanin kai harin ne Joe Biden ya gana da jami'an Amurka dake Iraqin, sai dai kuma wani mai magana da yawunsa ya ki fadin inda yake sabilida dalilan tsaro.


Tawagar 'yan majalissar kungiyar Tarayyar Afirka na ci gaba da ganawa da bangarori dabam-dabam a Niger, da zumar gano bakin zaren rikicin siyasar da ya dabaibaye kasar.

A yau jami'an Tarayyar Afirkan sun kwashe kimanin awoyi hudu suna tattaunawa da kawancan CFDR mai adawa da shirin tazarcen shugaba Tanja Mamadou.

Wannan dai shine karo na kusan biyar da kungiyoyi irinsu ECOWAS, da Tarayyar Turai da sauransu, ke aikewa da tawagogi zuwa Niger din, domin sasanta rikicin siyasar kasar.


A Lagos an samu an shawo kan wata gobarar da ta tashi a yau, a wani katafaren gida da jami'an tsaro na 'yan sanda da sojoji ke zaune, a unguwar Ikoyi.

'Yan kwana-kwana sun kwashe sama da sa'o'i ukku, kamin su samu su kashe gobarar.

Ba rahoton wani ya rasa ransa, to amma an yi hasarar dukiya mai waya. Kawo yanzu dai ba a san abinda ya janyo gobarar ba.


An yi jana'izar fitaccen lauyan nan, kuma mai fafutukar kare hakkin bil'adama a Nigeria, Cif Gani fawehinmi. An yi jana'izar ce a Ondo, jahar sa ta haihuwa.

Makwanni biyun da suka wuce ne Cif Gani ya rasu a Lagos, yana da shekaru saba'in da daya a duniya, bayan ya dade yana fama da rashin lafiya.


 
 
KA KUMA DUBA
 
 
Aika ìmel ga aboki   Wanda za a iya gurzawa
 
  Game da mu|Tuntube mu
 
BBC Copyright Logo
 
^^ Koma sama
 
  Labarai | Yanayi
 
  BBC News >> | BBC Sport >> | BBC Weather >> | BBC World Service >> | BBC Languages >>
 
  Taimako | Tuntube mu | Tsare Sirri