
Jami'an tsaron Najeriya
Hukumomin tsaro a jihar Filato ta Nijeriya sun bukaci al'ummar musulmi da kada su je wani masallacin idi da ke wani yanki da mabiya addinin kirista suka fi rinjaye a birnin Jos yayin hidimomin karamar Sallah ta bana saboda dalilai na tsaro.
Kakakin rundunar 'yan sandan jihar, DSP Abu Emmanuel, ya shaidawa BBC cewa an yanke wannan shawarar ce a lokacin wani taro da jami'an tsaro suka gudanar.
A cewarsa, ana takaddama a kan filin da musulmin ke yin Sallar Idi a ciki, kuma batun na gaban kotu don haka bai kamata a yi shisshigi game da batun ba.
Har yanzu dai kungiyar Jama'atu Izalatul Bidi'a Wa'ikamatussunnah, wacce ta mallaki filin, ba ta mai da martani game da batun ba.
A bara dai an samu tashin hankali a birnin na Jos bayan da wasu mabiya addinin kirista suka yi wa musulmi kawanya yayin da suke Sallar Idi a masallacin da ke hanyar Rukuba.













