bbc.co.uk navigation

Mun mai da hankali ga wadanda suka tsira —Iran

An sabunta: 12 ga Agusta, 2012 - An wallafa a 15:11 GMT

Mutanen da girgizar kasar Iran ta raba da gidajensu

Hukumomi a Iran sun ce abin da suka mayar da hankali a kai bayan mummunar girgizar kasar ranar Asabar shi ne samar da abinci da matsuguni ga dubban mutanen da suka tsira da rayukansu.

Ministar lafiya ta kasar, Marzieh Vahid-Dastjerdi, ta ce ana kokarin tabbatar da cewa an kula da lafiyar wadanda abin ya shafa.

“Baya ga asibitocin wucin-gadi da aka kakkafa, shugaban Jami'ar Horar da Likitoci ta Tabriz ya amince ya samar da ayyukan kula da lafiya a duk wani tanti da ke kauyukan da al'amarin ya shafa”, inji ta.

A halin yanzu dai an dan sassauta da aikin ceto kasancewar an gano akasarin mutanen kauyukan da girgizar kasar ta daidaita.

Fiye da mutane dari uku ne dai suka rasa rayukansu yayin da fiye da dubu biyu suka jikkata.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.