bbc.co.uk navigation

Dakarun Masar sun kama mutane tara a Sinai

An sabunta: 10 ga Agusta, 2012 - An wallafa a 15:10 GMT
dakarun Masar a yankin Sinai

dakarun Masar a yankin Sinai

Gidan talabijin na kasar Masar ya ce sojoji sun kama mutane tara a yankin Sinai, inda suka kara karfafa matakan tsaro.

An tsaurara matakan tsaron ne a yunkurin kawo karshen ayyukan masu fafutukar Islama da suka kafa sansanoni a wasu kauyuka dake iyakokin zirin Gaza da Ira'ila.

Rundunar Sojin Masar na ci gaba da kara jibge dakarun soji a yankin na Sinai, bayan wasu rahotani dake cewa sun kashe 'yan gwagwarmaya kimanin ashirin ranar Laraba, a matsayin ramuwar gayya kan kisan da aka yi wa sojoji goma sha shidda.

A Wata tattaunawa da Ministan harkokin cikin gida na kasar Ahmed Gamal Al-Deen yayi da shugabannin Larabawan kauye, sun amince za su ba wa sojoji da 'yan sanda hadin kai domin tabbatar da tsaro a iyakokin kasar.

Shugaban Kasar Masar, Muhammad Morsi, ya kori wasu manyan jami'an tsaron kasar, da kuma gwamnan Arewacin Sinai, a kokarin da gwamnatin ke yi na mayar da martani mai karfi a kan duk wanda ya nemi kalubalantar ikon gwamnati.

Sai dai wasu na nuna shakku kan ko daukar matakan soja, ko na korar wasu manyan jami'ai zasu yi tasiri a wannan yanki, wanda ake samun karuwar nuna kaifin kishin addini, da kuma karya doka.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.