bbc.co.uk navigation

Amurka ta kara kakaba wa Hizbullah takunkumi

An sabunta: 10 ga Agusta, 2012 - An wallafa a 19:53 GMT
Mayakan kungiyar Hizbullah

Amurka ta zargi mayakan kungiyar Hizbullah da taimakawa dakarun Syria

Amurka ta zargi kungiyar Hizbullah mai gwagwarmaya da makamai a Lebanon da bayar da horo, da shawarwari, da kuma tallafi ga gwamnatin Syria a yunkurinta na murkushe ’yan adawa.

Ta kuma zargi kungiyar ta Hizbullah da taimaka wa Dakarun Juyin Juya-Hali na Iran, wato Revolutionary Guard, wajen bayar da horo ga dakarun Syria.

Tuni dai Washington ta ayyana Hizbullah a matsayin kungiyar ’yan ta’adda, ta kuma sanar da kakaba mata sababbin takunkumi.

Sai dai kuma wakilin BBC a Washington ya ce wannan takunkumi na je-ka-na-yi-ka ne saboda kungiyar ta Hizbullah ba ta da kadara a Amurka.

Kakakin Fadar Gwamnatin Amurka ta White House, Jay Carney, ya ce “Abin da muke son cimmawa shi ne mu ci gaba da matsawa gwamnatin Assad lamba, mu ci gaba da mayar da ita saniyar-ware, mu kuma nuna cewa abokan Shugaba Assad kalilan ne suka rage—wato Iran da Hizbulla”.

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.