bbc.co.uk navigation

Akwai dakarun Birtaniya a Somalia

An sabunta: 26 ga Yuli, 2012 - An wallafa a 15:40 GMT

Taswirar Somalia

Ma'aikatar tsaron Burtaniya, a karon farko ta tabbatar cewa akwai wasu jami'an tsaronta a cikin kasar Somalia.

Ma'aikatar ta ce yanzu haka wasu jami'an sojinta goma suna aikin bada shawara a Hedkwatar rundinar kiyaye zaman lafiya ta kungiyar Tarayyar Afruka dake Mogadishu, babban birnin kasar ta Somalia.

Wakilin BBC ya ce wadannan jami'an na Burtaniya ba su da hurumin shiga yaki, amma wasu daga cikinsu sun kasance a garin Afgoye na Yammacin Mogadishu, mai mhuimmancin gaske, wanda sojojin gwamnati suka kwato daga hannun mayakan kungiyar al Shaba'ab a kwanakin baya.

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.