bbc.co.uk navigation

'Majalisar sojin Masar ba ta da hurumin rusa Majalisar Dokoki'

An sabunta: 16 ga Yuni, 2012 - An wallafa a 20:31 GMT
majalisar dokokin Masar

majalisar dokokin Masar

Babbar kungiyar siyasar Masar ta 'yan uwa Musulmi ta zargi majalisar mulkin soji da ketare iyakar ikonta bayan da ta rusa majalisar dokokin kasar.

Kungiyar tace sanarwar da majalisar ta bayar ranar Asabar ta rusa majalisar dokokin ba ta kan ka'ida domin a cewarta, sojojin ba su da hurumin bayar da wannan umarni.

Rusa majalisar dokokin dai ya biyo bayan hukuncin da babbar kotun Masar ta yanke ne cewa zaben majalisar dokokin ya sabawa doka kuma ya kamata a sake shi.

Wani kusa a majalisar dokokin ya shaida wa BBC cewa ya samu wasika daga majalisar mulkin sojan dake sanar da shi game da rusa majalisar.

An rusa majalisar dokokin ce yayin da al'umar kasar ta ke zaben shugaban kasa .

Ana fafatawa ne tsakanin tsohon Firayim Minista a zamanin shugaba Mubarak, Ahmed Shafiq, da Muhammed Morsi na kungiyar 'yan uwa musulmi.

Rahotanni daga Masar na nuna cewa jama'a ba su fito sosai ba a ranar farko ta zaben.

Ana danganta hakan da matsayin da galibin matasa suka dauka cewa babu na zabe tsakanin 'yan takarar biyu.

Matasan ne suka kasance gaba gaba a lokacin boren da yayi sandiyar kifar da gwamnatin Hosni Mubarak.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.