bbc.co.uk navigation

Masar: ana zaben shugaban kasa

An sabunta: 16 ga Yuni, 2012 - An wallafa a 05:51 GMT

Masu zanga-zanga a Masar

Al'ummar kasar Masar suna kada kuri'a a zagaye na biyu na zaben sabon Shugaban kasa wanda zai gaji Hosni Mubarak da aka hambaras bara.

Ana hasashen za a yi kankankan ne tsakanin 'yan takara biyu2 da suka rage tsohon Prime Minista Ahmed Shafiq da Mohammed Morsi na jam'iyyar Muslim Brotherhood.

Sojojin dake jan ragamar mulkin kasar a yanzu sun yi alkawarin mika mulki ga wanda ya yi nasara.

A dandalin Tahrir dake tsakiyar birnin Alkahira masu zanga-zanga na cigaba da hallara don nuna bacin-ransu, suna kalaman batanci ga gwamnatin mulkin sojin ta Masar.

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.