bbc.co.uk navigation

An nuna shakku kan sahihancin zaben Masar

An sabunta: 26 ga Mayu, 2012 - An wallafa a 19:58 GMT
Zaben kasar Masar

Zaben kasar Masar

Daya daga cikin 'yan takarar shugaban kasa a Masar da ba basuyi nasara ba a zagayen farko, Hamdeen Sabahi yayi kira da asake kirga wasu kuri'un da aka kada saboda acewar sa anyi magudi.

Wani kakakin sa ya ce zai shigar da kara ranar Lahadi don hana gudanar da zagaye na biyu na zaben.

A daya bangaren kuma, wanda ake cewa shi ne ya zo na biyu a zaben, kuma tsohon Praministan Masar, Ahmed Shafiq yace zamanin shugaba Mubarak ya wuce har abada.


"Yace abunda ya wuce ya wuce.

Bazamu yi fada da juna ba, zamu yi aiki ne tare kuma ina amfanin komawa zamanin da ya wuce.

An samu sauyi a Masar kuma babu wanda zai maida hannun agogo baya".


Tsohon shugaban Amurka, Jimmy Carter da ke jagorantar wata tawagar masu sa ido yace koda yake ba' a barsu sun je ko ina ba, amma ya gamsu da tsarin da aka yi

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2013 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.