bbc.co.uk navigation

Kungiyar agaji ta Red Cross ta sami shiga birnin Homs na Syria

An sabunta: 24 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 19:24 GMT
Birnin Homs

Birnin Homs

Kungiyar agaji ta Red Cross da kuma bangarenta na Syria yanzu haka suna birnin Homs na Syriar, inda suke tattaunawa da hukumomin birnin da kuma dakarun 'yan adawa domin fitar da wadanda suka jikkata kuma ke matukar bukatar kulawa.

Ba a dai bada karin bayani ba a kan hakan:

Wakiliyar BBC ta ce, “Kungiyar agajin ta Red Cross dai ba ta ba da cikakken bayani ba a kan lokacin da za ta soma kwashe wadanda suka jikkata daga birnin na Homs.

Yanzu haka dai akwai 'yan Syria da dama da kuma wasu 'yan jaridar kasashen yamma da ke matukar bukatar agaji.

Hakan tana aukuwa ne byan da sojin gwamnatin Syriar suka kwashe makonni suka luguden wuta a kan birnin na Homs, inda suke fuskantar turjiya daga masu fafitika.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.