bbc.co.uk navigation

Zabe a Senegal babu gudu ba- ja- da- baya- N'Diaye

An sabunta: 24 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 06:52 GMT
Abdoullaye Wade na Senegal

'Yan adawa a Senegal sun nemi Abdoullaye Wade ya sauka daga kan mulki


Firayim Ministan Kasar Senegal Sulaiman Ndene N'Diaye ya ce za a yi zaben Shugaban Kasar kamar yadda aka tsara a ranar lahadi.

Wasu kungiyoyin 'yan adawa sun nemi a dage zaben, sun kuma lashi takobin cewar za su sanya komai ya tsaya cik a Kasar idan har Shugaban Kasar Abdullahi Wade mai shekaru tamanin da biyar da haihuwa ya ki sauka daga kan mulki.

Yana takara ne karo na ukku sabanin wa'adi biyu da tsarin mulkin ya tanadar a Kasar.

Tsohon Shugaban Najeriya chief Olusegun Obasanjo yana ganawa da shugabannin 'yan adawar da suka hada da sanannen mawakin nan Yousuf Ndor, a kokarin sassauta zaman zullumin da ake ciki.

Kari a kan wannan labari

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.