bbc.co.uk navigation

Yau ake soma babban taro kan Somalia a birnin London

An sabunta: 23 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 07:10 GMT
Kasar Somalia

Taron Kasashen duniya akan rikicin Somalia

Yau ne za a fara wani taro na Kasashen duniya a London a game da makomar Kasar Somalia.

Wannan wani yunkuri ne da Firayim Ministan Burtaniya David Cameron ke jagoranta don nemo sabbin hanyoyin da za a kawo karshen yamutsi da yunwa da yakin basasar da aka shafe sama da shekaru ashirin ana gwabzawa a Kasar.

Wakilai na gwamnatin rikon-kwarya da Kungiyoyi daban-daban ne za su halarci taron, amma banda Kungiyar 'yan gwagwarmaya ta Al Shabab wadda ke da ikon mafi rinjayen tsakiya da kuma kudancin Kasar ta Somalia.

A waje daya kuma dakarun Habasha da taimakon sojan gwamnatin rikon kwaryar Somalia sun kwace ikon mulki da birnin Baidoa dake tsakiyar Kasar a hannun mayaka na Kungiyar Kishin Islama ta AlShabab.

Sun kwaci birnin ne salun-alun ba tare da wani fada ba lokacin da mayakan na Al Shabab suka arce daga yankin suna cewar maimakon fadan, za su koma yakin sari-ka-noke

To amma masu aiko da rahotanni sun ce hakan wani babban koma-baya ne ga Kungiyar ta AlShabab.

Kari a kan wannan labari

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.