
Kamfanin mai na Chevron ya ce, rijiyar man sa za ta ci gaba da ci da wuta har zuwa wani lokaci.
Katafaren kamfanin mai na Chevron ya shaidawa BBC cewar gobarar da ta afkawa wata rijiyar mai a tekun Nigeria a watan Janairun da ya gabata, akwai yiwuwar cewa za ta cigaba da ci da wuta a watanni masu zuwa.
Ma'aikatan kamfanin su biyu sun hallaka a lokacin da gobarar ta kama a rijiyar.
Wakilin BBC yace mahukuntan kasar Najeriyar sun cee iskar gas din da ta rika fita ita ce ta haddasa fashewar rijiyar mai wacce ta kama da wuta a tsakiyar watan da ya gabata.
Lamarin dai ana ganin cewa , ya hana al'ummar kauyen Kolouma cigaba da sana'ar su ta kamun kifi.









