bbc.co.uk navigation

Kasashen yammacin Afrika da Amurka suna atisaye a Gabar Ruwan Guinea

An sabunta: 21 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 20:54 GMT
Jiragen yaki

Jiragen yaki

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta fara gudanar da wani atisayen hadin gwiwa na kwanaki hudu tare da wasu kasashe goma sha uku da ke makwabtaka da tekun Atlantika, a Calabar da ke kudancin kasar.

Rahotanni na dai, nuna cewa atisayen, wanda kasar Amurka, da wasu kasashen Turai ke halarta, ana gudanar da shi ne don kara inganta harkokin tsaro a kasashen da ke makwabtaka da tekun Atlantika – yankin da ake kira Gabar Guinea ko kuma Gulf Of Guinea.

Ana dai yin wannan atisaye ne bayan kungiyar kula da sufurin jiragen ruwa ta kasa da kasa ke yi wa 'ya 'yanta kashedin akan amfani da tekun da ke kusa da Najeriya saboda karuwar ayukan 'yan fashin jiragen ruwa.

Bayan fashin, yankin yana kuma fama da wasu matsalolin da suka shafi ta’addanci.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.