bbc.co.uk navigation

Yawan 'yan gudun hijirar Mali ya rubanya

An sabunta: 17 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 23:36 GMT
'Yan gudun hijirar Mali

Wasu daga cikin 'yan gudun hijirar Mali a Yammacin Nijar

Majalisar Dinkin Duniya ta ce adadin ’yan kasar Mali wadanda ke gudun hijira zuwa kasashen da ke makwabtaka da su don gujewa fada tsakanin ’yan tawaye Abzinawa da sojin gwamnatin kasar ya rubanya a cikin kwanaki goman da suka wuce.

Yan gudun hijirar fiye da dubu arba'in da hudu ne suka ketara zuwa kasashen Mauritaniya da Nijar da Burkin Faso, inda a halin yanzu Hukumar Kula da ’Yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya ke yi musu rajista.

Kungiyar kare hakkin bil-Adama ta Amnesty International ta bayyana fadan, wanda ya barke a watan Janairu, da cewa shi ne bala’i mafi muni a kasar ta Mali a cikin shekaru ashirin.

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Yammacin Afirka, ECOWAS ko CEDEAO, ta yi Allah-wadai da harin da ’yan tawayen suka kaddamar.

Wakilin BBC a Yammacin Afirka ya ce yanzu kura ta dan lafa a yankin.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.