
Dama dai Lamurde babban jami'i ne a hukumar ta EFCC
Majalisar dattawan Najeriya ta amince da Ibrahim Lamurde a matsayin shugaban hukumar yaki da yiwa tattalin arzikin kasa ta'annati ta EFCC.
Lamurde ya maye gurbin tsohuwar shugabar hukumar Farida Waziri wacce aka kora daga aiki a watan Nuwamban bara.
Hakan ne kuma ya sa shugaba Goodluck Jonathan ne ya nada Mr Lamurde - wanda babban jami'i ne a hukumar domin shugabantar EFFC na wucin-gadi.
Amma daga bisani ya mika sunansa ga Majalisar dattawan domin neman amincewarta kan Mr Lamurde ya jagoranci hukumar a matsayin shugaba na din-din-din.









