bbc.co.uk navigation

Sojojin Syria na cigaba da kai hari a Homs

An sabunta: 9 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 15:56 GMT
Dan tawaye a Syria

Dan tawaye a Syria

Dakarun gwamnatin Syria sun sake kai sabbin hare haren bam a birnin Homs, a kwana na shidda a jere, a yunkurin da suke na murkushe 'yan tawaye.

Rahotanni sun ce, mutane 30 ne suka rasu a luguden wutar na yau.

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Ban Ki-moon, ya ce yana fargabar abubuwan rashin imanin da ke faruwa a birnin na Homs, somin tabi ne na halin o-ni-'yasun da za a shiga a nan gaba.

Masu fafitika sun ce, dakarun gwamnatin Syriar na kara daukar matakai a kan iyakokin kasar da kasashen Jordan da Lebanon da Turkiya da Iraki, domin hana shigar da makamai a Syriar don 'yan tawaye.

Jamus ta kori wasu ma'aikatan ofishin jakadancin Syria su hudu, bayan an kama wasu mutane biyu da ake zargi da yin leken asiri a kan kungiyoyin adawan Syria da ke zaune a kasar ta Jamus.

Kari a kan wannan labari

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.