bbc.co.uk navigation

An kaddamar da babban kamfanin siminti a Najeriya

An sabunta: 9 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 16:03 GMT
Aliko Dangote

Aliko Dangote

A Najeria an kaddamar da kamfanin simintin da aka ce shi ne mafi girma a yankin Afirka na kudu da hamadar Sahara, a garin Ibase na jahar Ogun.

Ana sa ran kamfanin, wanda mallakar hamshakin mai kudin nan ne, Alhaji Aliko Dangote, zai taimaka wajen rage matsalar karanci da tsadar simintin da ake fuskanta a Najeriya, da ma wasu kasashen Afirka.

Za a kuma samu ayyukan yi kimanin dubu goma.

Manyan jami'ai daga ciki da kuma wajen Najeriyar ne suka halarci bikin kaddamarwar, ciki har da shugaba Goodluck Jonathan.

Kari a kan wannan labari

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.