bbc.co.uk navigation

Rashin daukar mataki kan Syria masifa ce -Ban Ki Moon

An sabunta: 9 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 07:28 GMT

Ban Ki Moon

Babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Ban ki Moon, ya ce gazawar kwamatin sulhu na Majalisar wajen daukar mataki game da rikicin da ke faruwa a Syria, tamkar wata masifa ce ta fadawa 'yan kasar.

Mr Ban ya ce matakin zai karawa gwamnatin kasar kaimi wajen ci gaba da cin mutuncin 'ya'yanta.

Ya ce gwamnatin kasar ta kashe dubban 'ya'yanta wadanda ba su da laifi, amma duk da haka shugaban kasar Bashar al- Assad na ikirarin cewa yana kashe-kashen ne da yawun bakin 'yan kasar.

Mr Ban ya yi gargadin cewa luguden wutar da sojin gwamnatin kasar ke yi a birnin Homs na da matukar tayar da hankali, kuma ya nuna cewa gwamnatin shugaba Assad bata da niyyar kawo karshen rikcin da ke faruwa a kasar.

A ranar Asabar ne dai kasashen Rasha da China suka yi watsi da wani kuduri da kungiyar kasashen Larabawa ta gabatar wa kwamatin sulhun, wanda ya nemi yin Alla-wadai da rikicin da ke faruwa a kasar.

Kari a kan wannan labari

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.