bbc.co.uk navigation

Gwamnatin Nijar ta yi karin albashi, ta rage kudin ruwan famfo

An sabunta: 8 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 21:08 GMT

Gwamnatin Janhuriyar Nigar ta bada sanarwar karin albashi ga ma'aikatanta tare da rage kudin ruwa da na wutar lantarki.

A cewar gwamnatin wannan wani kokari ne na yaki da cin hanci da rashawa kamar yadda shugaba Muhammadou Issaoufo ya yi alkawarin yi a lokacin yakin neman zabensa.

A na dai daukar Niger din a matsayin kasar da bata da wadata, koda yake tana da arzukin yuranium ga kuma man fetur din da ta fara tonowa a karshen shekarar da ta gabata.

To ko mai yasa gwamnatin Niger ta dauki matakin karawa ma'aikatan kasar albashi? Wannan itace tambayar da naiwa kakakin gwamnatin Marou Amadou:

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.