bbc.co.uk navigation

Gwamnatin Ghana ta janye karin farashin mai

An sabunta: 6 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 16:29 GMT
Shugaba John Atta Mills

Shugaba John Atta Mills

Gwamnatin Ghana ta ba da sanarwar janye karin farashin man petur.

Hakan ya zo yayin da hadaddiyar kungiyar kwadagon kasar, wato TUC, ke
shirin fara wani yajin aikin gama-gari, don nuna adawa da karin da gwamnatin ta yi.

Watanni biyu kenan da gwamnatin ta yi karin kashi 20 cikin 100 ga farashin man fetur din.

Gwamnatin Ghanar dai ta janye sabon farashin ne, bayan wata ganawa da mataimakin shugaban kasar, Mr John Mahama ya yi da shugabannin kungiyar kwadagon kasar, a karshen makon jiya.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.