bbc.co.uk navigation

MEND ta fasa bututun mai na Agip

An sabunta: 5 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 20:12 GMT
Masu fafutukar yankin Niger Delta

Masu fafutukar yankin Niger Delta

A Najeriya, kungiyar MEND mai fafutuka a yankin Niger Delta ta ce, ita ce ta kai hari akan wani bututun mai, mallakar kamfanin AGIP na Italiya.

Shaidu sun ce, a daren jiya sun ga wuta na tashi daga bututun man Nembe-Brass, a jahar Bayelsa.

Kamfanin man na AGIP dai bai ce komi ba game da lamarin.

Kungiyar MEND ta kwashe shekaru tana yiwa masana'antun mai zagon kasa a yankin na Niger Delta.

To amma ta yi sanyi tun bayan da ta karbi ahuwar da gwamnatin tarayya ta yiwa masu fafutuka, a shekara ta 2009.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.