bbc.co.uk navigation

An kashe fiye da mutane dari biyu a birnin Homs

An sabunta: 4 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 15:25 GMT
An kai farmaki a Homs

An kai farmaki a Homs

Masu fafutuka a Syria sun ce, fiye da mutane dari biyu sun hallaka, a wani farmakin da sojojin gwamnati suka kai a birnin Homs.

Gwamnatin Syria dai ta musanta cewa dakarunta sun yi barin wuta a Homs din.

Ta kuma dora alhakin kashe kashen akan wadanda ta kira, kungiyoyin 'yan ta'adda masu dauke da makamai.

Can kuma a majalisar dinkin duniya, ministan harkokin wajen Rasha, Sergei Lavrov, ya ce, abin kunya ne idan har a yau, majalisar ta kada kuri'ar amincewa da wani daftarin kuduri, mai yin Allah wadai da tashe tashen hankulan da ke faruwa a Syriar.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.