bbc.co.uk navigation

Ana ci gaba da zaben gwamna a jahar Adamawa

An sabunta: 4 ga Fabrairu, 2012 - An wallafa a 15:48 GMT
Ana zaben gwamma a jahar Adamawa

Ana zaben gwamma a jahar Adamawa

A Najeriya yanzu haka jama'a a jahar Adamawa na ci gaba da kada kuri'ar zaben gwamnan jahar, karkashin tsauraran matakan tsaro.

Tuni dai aka tsaurara matakan tsaro inda aka girke dubban jami'an tsaro ciki har da wadanda aka tura jihar daga wasu jihohin kasar, domin kula da sha'anin tsaro a lokacin zaben.

Ana ganin fafawa tafi zafi tsakanin Vice Admiral Murtala Nyako mai ritaya, na jam'iyyar PDP, da kuma tsohon gwamnan mulkin soja a jihar Lagos, Birgediya Janar, Buba Marwa mai ritaya, na jam'iyyar CPC.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.