Gwamnatin Afghanistan za ta tattauna da Taleban a Sa'udiya

An sabunta: 29 ga Janairu, 2012 - An wallafa a 15:44 GMT
Shugaba Hamid Karzai

Ko a wannan karon Taleban za ta amsa kiransa?

BBC ta samu labarin cewa gwamnatin Afghanistan na shirin ganawa da kungiyar Taliban a kasar Saudiyya cikin 'yan makwanni masu zuwa.

Tattaunawar, wadda ita ce irinta ta farko, wani muhimmin abu ne a kokarin da ake yi na samun hanyar warware rikicin Afghanistan.

Abu na baya-bayan nan da aka maida hankali a kai shi ne na kokarin da Amurka ke yi domin ganawa da 'yan Taliban din, wadanda ke son kafa wani ofishi a Qatar:

Wakiliyar BBC ta ce shugaba Hamd Karzai ya ji haushin kokarin da Amurka da Qatar ke yi na tattaunawa da Taliban ba tare da tuntubar gwamnatinsa ba.

Shugaban kasar Afghanistan, Hamid Karzai, ya ce ya kamata Afghanistan ce za ta jagoranci tattaunawar zaman lafiyar, sai dai a baya kungiyar Taliban ta gwasale gwamnatinsa, wadda take dauka a matsayin haramtacciya.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

bbc.co.uk navigation

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.