bbc.co.uk navigation

Shekau ya amsa cewa su suka kai hare-hare a Kano

An sabunta: 26 ga Janairu, 2012 - An wallafa a 17:55 GMT
 Malam Abubakar Shekau

Malam Abubakar Shekau

Kungiyar nan ta Ahlus Sunna Lid-Da'awati wal Jihad, wadda aka fi sani da Boko Haram ta sake fitar da wani sako na murya mai kunshe da muryar Shugaban Kungiyar, Imam Abubakar Shekau a dandalin sakonnin bidiyo na You-tube.

Shugaban Kungiyar, wanda ke sanye da farar riga da rigar sulke dauke da bindiga, ya yi jawabi na kusan minti arba'in a wannan bidiyo, inda yake bayyana cewa kungiyar ce ta kai hari ranar Juma'a a Kano, al'amarin da ya haddasa mutuwar mutane akalla dari da tamanin da biyar.

Shugaban Kungiyar ya kuma kara yin gargadi ga mahukuntan Nigeriya da su guji kai masu hare hare da kokarin kama masu magoya baya.

Ya zargi jami'an tsaron Nijeriya da bindige fararen hula, bayan 'yan kungiyarsu sun kammala kai hare hare a birnin na Kano.

Malam Shekau ya kuma kawara da yuwuwar shiga wata tattaunawar sulhu da hukumomin Nijeriyar.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.