bbc.co.uk navigation

Kokarin daidaita al'ammura a Sudan ta Kudu

An sabunta: 30 ga Disamba, 2011 - An wallafa a 15:56 GMT
Wani makiyayi a Sudan ta Kudu

Wani makiyayi a Sudan ta Kudu

Majalisar Dinkin Duniya ta tura wata rundunar zaratan sojoji zuwa garin Pibor dake Sudan ta Kudu domin hana barkewar rikici tsakanin kabilu biyu da ke gaba da juna.

Kimanin 'yan bindiga dubu shida ne daga kabilar Lo Nuwar ke yin kutse cikin jahar Jonglei suna kona gidaje suna kuma kwace shanun 'yan kabilar Murle.

Wakilin BBC ya ce a 'yan sa'o'in da suka wuce dubban 'yan kabilar Murle sun tsere daga garin Pibor suna fargabar kawo musu hari.

Shugaban ofishin Majalisar Dinkin Duniya da ke Sudan ta Kudu, Lise Grande ya shaidawa BBC cewa MDD ta tura sojoji zuwa Pibor domin su taimaka wa dakarun sojin Sudan ta Kudun.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.