bbc.co.uk navigation

'Yan Taliban za su bude Ofis a Qatar

An sabunta: 27 ga Disamba, 2011 - An wallafa a 20:48 GMT
Shugaba Hamid Karzai

Shugaba Hamid Karzai

Shugaban Afghanistan Hamid Karzai ya ce zai kyale 'yan kungiyar Taliban su bude ofis a kasar Qatar,a wani yunkuri na taimakawa shirin wanzar da zaman lafiya.

Wannan dai shi ne karon farko da shugaba Karzai ya nuna goyon bayansa a bainar jamaa ga wannan batu.

Sai dai fadar shugaban ta ce ya kamata a hana duk wata kasar waje yin katsalanda a tattaunawar zaman lafiya.

A kwanan nan dai wasu rahotannin sun nuna cewa Amirka da wasu kasashe dake sojoji a kasar ta Afghanistan, suna kokarin yin tasu tattaunawar ta dabam da 'yan Taliban .

Kawo yanzu dai kungiyar ta Taliban ba ta ce uffan game da wannan batu ba.

Kari a kan wannan labari

Maudu'o'i masu alaka

BBC © 2012 BBC ba ta da alhakin abubuwan da ke kunshe a shafukan da ba nata ba.

Wannan shafin zai fi kyan gani, idan an shige shi da browser mai salo na bai daya. Yayinda za ka iya samun damar duba abin da wannan shafin ya kunsa a browser da kake da ita a halin yanzu, ba za ka samu damar ganin dukkan abin da shafin ya kunsa kamar yadda ya kamata ba. Dubi yiwuwar inganta manhajar browsar ka, ko kuma ka samu browser mai salo na bai daya, idan har za ka iya.